Ranar Talata za a yi babbar sallah a Najeriya

[ad_1]

Ganin wata

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Babban kwamitin ganin wata a Najeriya ya fitar da wata sanarwa da ke cewa ranar Talata 21 ga wannan watan ne ranar babbar Sallah a Najeriya.

Kwamitin ya fitar da sanarwar ne a shafinsa na Twitter, inda ya bayyana dalilinsa na yin haka:

“A kan batun cewa Saudiyya ta bayyana ranar Dhl Hijjah da ta bambanta da wanda muka riga muka bayyana, kwamitin ganin wata ya tuntubi babban kwamitin Fatawa na kasa a shekarun baya, kuma an fitar da wata Fatawa mai cewa ya kamata mu rika bin hukuncin ganin watan da kasar Saudiyya ta yanke na Dhul Hijjah saboda muhimmancin hawan Arafat.”

Wannan sanarwar ta ci karo da sanarwar farko da kwamitin ya fitar.

Sanarwar kwamitin ta cigaba da cewa, “A kan haka ne Mai Alfarma Sarkin Musulmi, bayan ya tuntubi kwamitin Fatawa da kwamitin ganin wata da sauran malaman addini har da sarakunan gargajiya, ya bayyana Lahadi 12 ga watan Agusta 2018 a matsayin 1 ga watan Dhul Hijjah 1439H.”

A sanadiyyar wannan sauyin, mutane da dama sun fito suna maganganu na nuna rashin gamsuwa da matakin da kwamitin ya dauka.

A shafin kwamitin na Twitter, wasu sun soki wanann mataki:

Hamma @HAHayatu ya bayyana rashin jin dadinsa, “Kamata yayi ku amince cewa bamu fara azumin bana a kan lokaci ba, kuma kwanaki tsakanin Eid el Fitir da Eid al Adha ba sa wuce 70, kuma ba sa kasa 67. Mutane da dama sun ga watan a wurare masu yawa, amma kuka ki amincewa da haka.”

Shi ma Osama Ibraheem @GmIBRAHEEM cewa yayi, “Dama mun san haka za kuyi tun bayan ganin wata Zhul Qada, watan Shawwal bai cika kwana 30 ba, kuma kun yi ta gardama da mu a cikn wannan zauren. Ku koma ku duba, zaku tabbatar da abin da nake cewa.”

Amma wani mutumin mai suna Simwal @Simwal ya bayyana cewa ba Najeriya ce kawai ta sauya ranar babbar sallah ba.

Ya saka wata sanarwa daga mahukuntan Oman da ke bayyana haka:

“Daular Oman ta sauya ranar 29 ga watan Dhul Qadah ta koma 1 ga watan Dhul Hijjah a hukumance saboda sanarwar da Saudiyya ta fitar.”

A nasu bangaren kwamitin ganin watan ya kare kansa daga dukkan zargin da ake ke yi masa.

“Allah zai tambayemu dukkan abubuwan da muka aikata. Masu cewa an ga wata amma mun ki amincewa da bayanansu, kamata yayi su gabatar mana da hujjojinsu – a shirye muke da mu duba. Idan aka hada kwana 30 na Shawwal da 28 na Dhul Qadah da kuma kwana 10 na Dhul Hijjah sun kasance kwana 68 kenan.”



[ad_2]

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...