Ranar Litinin za a sake  bude ginin ofishin jam’iyyar PDP da aka rufe

Samuel Anyanwu sakataren tsagin jam’iyar PDP dake biyayya ga  ministan birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce za a sake buɗe ginin sakatariyar jam’iyar a ranar Litinin.

Anyanwu ya bayyana haka ne bayan taron da hukumar zabe mai zaman kanta ta ƙasa INEC ta yi da jam’iyyun siyasa inda tsagin ya wakilci PDP a wurin taron.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN ya rawaito cewa a ranar 19 ga watan Nuwamba ne jami’an ƴan sanda suka rufe ginin ofishin jam’iyyar biyo bayan hayaniyar da aka yi tsakanin bangarorin biyu na jam’iyar da suka haɗa da tsagin shugabancin Tanimu Turaki da kuma na Abdulrahaman Muhammad.

Da aka tambaye shi me yasa har yanzu shugabannin jam’iyar ba su karbi iko da ginin Wadata  Plaza ba Anyanwu  ya ce an rufe ginin ofishin ne bayan rikici a tsakanin bangarorin biyu

“Mun rubatawa yan sanda takarda.Idan za a tuna yan sanda ne suka rufe ofishin su kuma ɗaya ɓangaren suka tafi kotu neman umarnin yan sanda su buɗe musu,” ya ce .

“An kori karar saboda basu da hujja.saboda haka ranar Litinin zamu karɓe iko da ginin.”

More from this stream

Recomended