Ranar Bikin Matasa Ta Duniya

[ad_1]

Majalisar Dinkin Duniya, MDD, ta ware duk ranar 12 ga watan Agusta a matsayin ranar matasa, don duba ga matsaloli da kuma hanyoyin warware su a fadin Duniya.

Wakilin Muryar Amurka ya zagaya birnin Ibadan, inda ya zanta da matasa domin jin wane irin matsaloli suke fuskanta. Yawancin matasan da suka yi magana sun nuna rashin jin dadinsu ga rashin kulawar da ake musu.

Babbar matsalar da ke damun matasan dai ba ta wuce rashin samun aiyukan yi ba, wanda suke nemi shugabanni da su tashi tsaye wajen samar da ayyukan yi da zasu basu damar samun rayuwa mai inganci.

A wannan zamani dai wasu ‘yan siyasa na amfani da matasan wajen basu kudi da tsunduma su cikin bangar siyasa.

Domin karin bayani saurari rahotan Hassan Umaru Tambuwal.

[ad_2]

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...