Ranar Bikin Matasa Ta Duniya

[ad_1]

Majalisar Dinkin Duniya, MDD, ta ware duk ranar 12 ga watan Agusta a matsayin ranar matasa, don duba ga matsaloli da kuma hanyoyin warware su a fadin Duniya.

Wakilin Muryar Amurka ya zagaya birnin Ibadan, inda ya zanta da matasa domin jin wane irin matsaloli suke fuskanta. Yawancin matasan da suka yi magana sun nuna rashin jin dadinsu ga rashin kulawar da ake musu.

Babbar matsalar da ke damun matasan dai ba ta wuce rashin samun aiyukan yi ba, wanda suke nemi shugabanni da su tashi tsaye wajen samar da ayyukan yi da zasu basu damar samun rayuwa mai inganci.

A wannan zamani dai wasu ‘yan siyasa na amfani da matasan wajen basu kudi da tsunduma su cikin bangar siyasa.

Domin karin bayani saurari rahotan Hassan Umaru Tambuwal.

[ad_2]

More News

ÆŠalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...