Ramadan: Sarkin Musulmi Ya Ayyaana Laraba A Matsayin Ranar Fara Azumi

Muhammad Sa’ad Abubakar, Sarkin Musulmi, ya ayyana ranar Laraba 18 ga watan Fabrairu, 2026 a matsayin ranar farko ta watan Azumin Ramadan na shekarar 1447 Hijira, bayan tabbatar da ganin jinjirin watan.

Sanarwar ta fito ne cikin wata takarda da Sambo Wali Junaidu, Wazirin Sakkwato kuma Shugaban Kwamitin Shawara kan Harkokin Addini na Majalisar Masarautar Sakkwato ya sanya wa hannu.

A cewar sanarwar, rahotanni daga kwamitocin ganin wata na ƙasa daban-daban sun tabbatar da ganin jinjirin watan a ranar Talata 17 ga watan Fabrairu, wadda ta kasance rana ta 29 ga watan Sha’aban 1447 Hijira.

Bayan amincewa da rahotannin, Sarkin Musulmin, wanda shi ne Shugaban Ƙungiyar Nigerian Supreme Council for Islamic Affairs (NSCIA), ya sanar da Laraba a hukumance a matsayin ranar fara azumi.

Sarkin Musulmin ya taya al’ummar Musulmi murna tare da yin addu’ar neman shiriya da albarkar Allah a tsawon watan. Haka kuma ya bukaci Musulmi da su yi amfani da wannan lokaci wajen yin addu’o’in zaman lafiya, ci gaba da bunƙasar ƙasa.

Ya kuma yi fatan alheri ga daukacin Musulmi, yana roƙon Allah (SWT) Ya karɓi ibadu, tare da yi musu fatan Ramadan Kareem mai albarka.

More from this stream

Recomended