Qatar Da Sauran Kasashen Larabawa Sun Ce Sun Dakile Hare-Haren Iran

Rundunar sojin Qatar ta tabbatar da cewa Iran ta kai hare-hare a ƙasar, inda Amurka ke da sansanin sojin sama na Al-Udeid Air Base, mafi girma da take da shi a yankin Gabas ta Tsakiya.

Sai dai hukumomin Qatar sun ce sun samu nasarar kakkaɓo hare-haren ba tare da an samu wata babbar illa ba.

A Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ma, hukumomi sun tabbatar da mutuwar mutum guda bayan da aka dakile wani hari da ake zargin Iran ta kai.

Haka kuma, Bahrain ta ce an kai hari kan sansanonin sojin ruwan Amurka da ke ƙasarta, duk da cewa ba ta danganta harin da wata ƙasa ba.

Ita ma Kuwait ta bayyana cewa ta yi nasarar kakkaɓo wani hari da aka kai kan sansanin sojin Amurka da ke ƙasar.

Lamarin na nuni da ƙarin tashin hankali a yankin Gabas ta Tsakiya, yayin da hare-haren ke ƙara yaɗuwa tsakanin ƙasashe.

More from this stream

Recomended