PDP Tana Shirin Kai Wa Sanatocinmu Hari — APC

[ad_1]








Jam’iyyar APC ta zargi PDP da gudanar da shirye-sharyen kai farmaki ga Sanatocin APC. Hakan na cikin yun’kurinsu na tabbatar da cewa Sanata Bukola Saraki ya ci gaba da kasancewa Shugaban Majalisar Dattawa.

A wani jawabi da jam’iyyar APC ta fitar ta bakin sakataran ri’ko na watsa labaran jam’iyyar na ‘kasa, Mista Yekini Nabena, ta yi kira ga hukumomin tsaro da su samar da kariya ga Sanatocin.

“Jam’iyyar PDP da Saraki za a kama kai-tsaye idan har aka lahanta kowanne Sanata. Muna kira ga hukumomin tsaro da su kuma sanya ido a kan aikace-aikacen wasu daga cikin shuwagabannin PDP, ciki har da Saraki Saboda shirin kai wa Sanatocin APC hari gaskiya ne kuma gab yake da zuwa.”

Jam’iyyar ta kuma bayyana cewa an shirya ma’kar’kashiyar a daren Lahadi a gidan wani Shugaban PDP da ke Maitama-Abuja. Ta ‘kara da faɗin cewa mitin ɗin ya samu halartar wasu Sanatoci ‘yan koron Saraki guda 15 da kuma shi kanshi Shugaban Majalisar Dattawan.

APC ta bayyana cewa Sanatocin PDP sun tsara hare-hare masu yawa. D’aya daga cikinsu shi ne yun’kurin yaudarar wasu daga cikin Sanatocin APC zuwa wani waje a cikin dare ta hanyar gayyatarsu wani taron sulhun siyasa. Ana cikin mitin ɗin sai a ‘kir’kiro wata tarzoma. Daga nan sai kawai a sanya ‘yan daba su ‘kaddamar wa Sanatocin APC ɗin.




[ad_2]

More News

Ƴansanda sun kama muggan ƴan fashi da makami

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Elemoro reshen jihar Legas sun kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a fashi da makami a...

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riƙaƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 ƙirar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...