PDP ta lashe zaben Kuros Riba

[ad_1]

Voting in process in Nigeria

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Dan takarar jam’iyyar PDP ya lashe zaben maye gurbi na mazabar Obudu, inda ya doke sauran ‘yan takara daga jam’iyyu hudu.

Dan takarar jam’iyyar PDP, Abbey Awara Ukpukpen ya lashe zaben da kuri’u 12, 712.

Ya doke sauran ‘yan takarar da suka fafata da shi, ciki har da na jam’iyyar APC wanda ya sami kuri’u 4,345.

An dai gudanar da zabuka guda hudu na maye gurbi a wasu mazabu dake ciki tarayyar Najeriya a jiya Asabar.

Mazabun sune na sanatoci a Arewacin Katsina da Kudancin Bauchi da na dan majalisar wakilai a mazabar Lokoja/Kogi Koton-Karfe na jihar Kogi.

Akwai kuma zaben maye gurbin dan majalisar jiha a mazabar Obudu ta jihar Kuros Riba.

[ad_2]

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...