PDP ta ɗauki hanyar warware rikicin jam’iyar

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad ya ce  an kawo karshen rikicin cikin gida da ya dabaibaye jami’yar PDP.

Mohammed wanda shi ne shugaban ƙungiyar gwamnonin jam’iyar PDP ya bayyana haka ne a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe dake Abuja lokacin da yake magana da yan jaridu a ranar Talata.

Shugaban riƙo na jam’iyar PDP, Umar Damagum tare da wasu mambobin jam’iyar na tare da gwamnan lokacin da yake jawabi.

Mohammed ya ce gwamnonin jam’iyar da  kwamitin amitattun jam’iyar sun umarci shugaban cin jam’iyar na baya da Damagum ke jagoranta da su cigaba da jan ragamar jam’iyar.

” Ina so na sanar muku a madadin kungiyar gwamnonin jam’iyar PDP, shugaban sanatocin jam’iyar PDP da kuma wakilin kwamitin amitattun jam’iyar. Mun gudanar da taro a matsayin mu na iyali guda muna so mu sake tabbatar da cewa babu wani tsagi a jam’iyar PDP, ” Muhammad ya ce .

“Duk wani batun dakatar wa da kuka ji a baya a yanzu gwamnoni sun warware wannan,”

Ya ƙara da cewa babu wata jam’iya da bata da matsala wasu na shari’a ne kuma bama san yin riga malam masallaci kan abun da hukuncin zai ce.

More News

Magoya bayan jam’iyar NNPP sun ƙona jar hula

Wasu daga cikin mambobin wani tsagi na jam'iyar NNPP sun barranta kansu da jagoran jam'iyar na ƙasa, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso inda suka riƙa...

Magoya bayan jam’iyar NNPP sun ƙona jar hula

Wasu daga cikin mambobin wani tsagi na jam'iyar NNPP sun barranta kansu da jagoran jam'iyar na ƙasa, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso inda suka riƙa...

Dakarun Najeriya sun cafke wasu ƴan’aiken ƴanbindiga a Kaduna

Sojoji sun kama wasu mutum biyu da ake zargi da kaiwa 'yan bindiga sakonninsu a kasuwar ƙauyen SCC da ke ƙaramar hukumar Kachia a...

An gano gawar wani jami’in tsaro a ɗakinsa a Abuja

A gano gawar wani mataimakin Sifiritandan Ƴan sanda  Musa Yakubu dake aiki da ofishin ƴan sanda na Yaba a karamar hukumar Abaji dake birnin...