PDP 2019 – Atiku ne zai kara da Buhari a 2019

Babbar jam’iyyar adawa a Najeriya, PDP, ta zabi tsohon mataimakin shugaban kasar Atiku Abubakar a matsayin wanda zai kalubalanci shugaban Muhammadu Buhari na jam’iyyar APC a zaben da za a yi a watan Fabrairun 2019.

Alhaji Atiku Abubakar, ya samu takarar ne bayan ya samu nasara a kan abokan takararsa 11 wanda suma suka tsaya neman kujerar shugabancin Najeriyar a PDP.

Dan takarar shugabancin jam’iyyar na PDP, ya samu nasara ne da kuri’u 1532.

An dai gudanar da zaben ne a Fatakwal, babban birnin jihar Rivers inda wakilai da dama daga jihohin Najeriya 36 suka hallara domin zabar dan takarar da zai yi gogayya da shugaba Muhammadu Buhari.

Sauran ‘yan takarar da suka nemi kejarar shugabancin Najeriyar a jam’iyyar PDP, sun hadar da:

  • Jonah Jang da ya samu kuri’u 19
  • Datti Baba ya samu kuri’u 5
  • David Mark kuri’u 35
  • Turaki Taminu kuri’u 65
  • Sule Lamido kuri’u 96
  • Bafarawa kuri’u 48
  • Dankwabo 111
  • Ahmed Markafi kuri’u 74
  • Kwankwaso kuri’u 158
  • Olubukola Saraki kuri’u 317
  • Aminu Tambuwal kuri’u 693

Jam’iyyun siyasar ta Najeriya, sun kammala zaben ‘yan takararsu ne a yayin da a ranar Lahadin nan ne wa’adin da hukumar zaben Najeriya INEC ta ba jam’iyyu su mika sunayen ‘yan takara ke cika.

More News

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...

Mutane 18 sun ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota

Aƙalla fasinjoji 18 ne suka ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota da ya faru akan babbar hanyar Ojebu-Ode zuwa Ore a yankin Ogbere dake...

AMBALIYA: Bafarawa ya ba wa al’ummar Sokoto gudunmawar naira biliyan 1

Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Alhaji Attahiru Bafarawa, ya bayar da gudummawar Naira biliyan daya ga al’ummar Sokoto, domin rage radadin wannan annoba.An bayyana hakan...

Ƴanbindiga sun kai hari coci-coci a Kaduna, sun kuma yi garkuwa da mutane

Mutane 3 ne ake fargabar sun mutu, sannan an yi garkuwa da wasu 30 bayan wani hari da wasu ‘yan bindiga suka kai a...