Oshiomhole Ya Ziyarci Tinubu, Ya Yabi Girmamawar Da Amaryar Shugaban Kasa Ta Samu Daga Trump

Tsohon Gwamnan Jihar Edo kuma Sanata mai wakiltar Edo Arewa, Adams Oshiomhole, ya ziyarci Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu a fadar shugaban kasa a Abuja ranar Juma’a.

Bayan ganawarsu, Oshiomhole ya bayyana wa ‘yan jarida cewa ya zo fadar ne domin taya Shugaban Kasa barka da sabuwar shekara, inda ya kara da cewa bai hadu da Tinubu ba tun shekarar 2016. “Na zo domin taya shi murnar sabuwar shekara,” in ji shi.

Sai dai Oshiomhole ya kuma jaddada muhimmancin girmamawar da Amaryar Shugaban Kasa, Remi Tinubu, ta samu daga Shugaba Donald Trump na Amurka a taron National Prayer Breakfast.

“Jiya, mun ga yadda Shugaba Donald Trump ya girmama ba kawai Shugaban Kasa ba, har da uwargidansa, yana bayyana ta a matsayin mace mai daraja, mai sanin ya-kamata, kuma mai wa’azi a babban coci a Najeriya,” in ji Oshiomhole.

Ya ce wannan girmamawa na da muhimmanci, yana mai cewa: “A matsayin dan Najeriya, na ji alfahari. Muna ganin ya dace mu taya Shugaban Kasa murna, domin idan akasin haka ne, za ka ga yadda ‘yan adawa za su yi magana.”

Oshiomhole ya kara da cewa wannan alamar tana nuna muhimmancin hadin kai a tsakanin addinai a shugabancin Najeriya, inda ya ce: “Trump ya gane cewa Shugaban Najeriya Musulmi ne, kuma yana da mata Kirista wadda take mai wa’azi. Wannan yana nuna cewa ba za a samu rashin jituwa tsakanin Alkur’ani da Littafi Mai Tsarki ba, kuma ‘yan Najeriya su hada hannu domin ci gaban kasa.”

More from this stream

Recomended