Shugaban jam’iyar APC na kasa, Adam Oshimhole na so a tsige Yakubu Dogara daga muƙaminsa na shugaban majalisar wakilai ta tarayya.
Wata majiya ta shedawa jaridar The Cable cewa shugaban jam’iyar ya gana da yan jam’iyyar musamman wadanda suke majalisar wakilai a kokarin da yake na kawar da Dogara.
Majiyar ta ce shugaban na APC ya zage damtse wajen cire kakakin majalisar bayan da labari ya bazu cewa zai sake tsayawa takara a karkashin jam’iyyar PDP.
Wasu daga cikin mutanen mazabarsa sun mika masa fom din tsayawa takara a karkashin jam’iyar PDP a ranar Alhamis inda suka shawarce shi ya fice daga jam’iyar APC.
Har yanzu Dogara bai fito fili ba ya bayyana ficewarsa daga jam’iyar ta APC duk da cewa baya halartar tarurrukan jam’iyar.