Oshimhole na shirya yadda za a tsige Dogara

Shugaban jam’iyar APC na kasa, Adam Oshimhole na so a tsige Yakubu Dogara daga muƙaminsa na shugaban majalisar wakilai ta tarayya.

Wata majiya ta shedawa jaridar The Cable cewa shugaban jam’iyar ya gana da yan jam’iyyar musamman wadanda suke majalisar wakilai a kokarin da yake na kawar da Dogara.

Majiyar ta ce shugaban na APC ya zage damtse wajen cire kakakin majalisar bayan da labari ya bazu cewa zai sake tsayawa takara a karkashin jam’iyyar PDP.

Wasu daga cikin mutanen mazabarsa sun mika masa fom din tsayawa takara a karkashin jam’iyar PDP a ranar Alhamis inda suka shawarce shi ya fice daga jam’iyar APC.

Har yanzu Dogara bai fito fili ba ya bayyana ficewarsa daga jam’iyar ta APC duk da cewa baya halartar tarurrukan jam’iyar.

More News

Ƴansanda sun kama muggan ƴan fashi da makami

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Elemoro reshen jihar Legas sun kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a fashi da makami a...

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riÆ™aƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 Æ™irar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...