[ad_1]
Shugaba Muhammad Buhari ya tabbatar da cewa a bisa taimakon kasar China, Nijeriya ta samu damar aiwatar da ayyukan raya kasa daban daban da kudinsu ya kai Naira Tiriliyan biyu.
Buhari ya yi wannan ikirarin ne a yayin wata tattaunawa na mahalarta taron hadin guiwa na kasashen Afrika da China ( FOCAC) inda ya nuna cewa daga cikin wadannan ayyuka har da aikin hanyar jirgin kasa na Kaduna zuwa Abuja wanda aka yi amfani da sabon fasahar da China ta kirkiro.
[ad_2]