[ad_1]
Gamayyar kamfanonin da ke samarwa da raba wutar lantarki a Nijeriya (GENCos) sun gargadi hukumomin kasar game da yiwuwar shiga matsalar samun wutar lantarki.
A wata sanarwa da babban sakatariyar daya daga cikin kungiyoyin da ke cikin gamayyar, APGC, Joy Ogaji ta aikawa manema labarai a jiya Alhamis, ta bayyana cewa gaba daya injinan samar da wutarsu na ta haska danjojin da ke nuna cewa a kowane lokaci za su iya daina aiki.
Ta ce wannan abu na faruwa ne saboda Kamfanin Raba Wuta na Nijeriya, TCN, ya kasa jan adadin wutar da ya kamata ya ja ya kai cikin tashar tattara wutar lankarki ta kasa, wato National grid.
Ta ce ko a watan Afrilu, an samu karfin wuta kimanin megawat 7,485, amma TCN 3985 kawai ta iya zuka ta raba.
Wannan dalilin ne ya sa injinan ke fuskantar matsala. A cewar Ogoji injinan kamar kayan wuta suke, idan wuta ta yi musu kadan, ba za su iya aiki ba. Idan kuma ta yi musu yawa, za su lalace.
[ad_2]