Nigeria Za Ta Karbo Bashin Dala Milyan 150 Domin Yakar Cutar Polio

[ad_1]

Majalisar zartaswar Nigeria ta amince da karbo lamunin dalar Amurka miliyan 150 daga bankin duniya a kokarinta na ci gaba da yaki da cutar polio.

Har yanzu ana fama da cutar polio a Nigeria sanadiyar kin amincewa da allurar rigakafi da wasu iyayen yara ke yi, da kuma matsalolin tsaro lamuran dake kawowa hukumomin kiwon lafiyar kasa cikas a wurin yaki da cutar polio.

A baya bayan nan kasar ta shawo kan matasalar ta hanyar wayar da kawunan jama’a da kuma jaddada mahimmancin rigakafin.

Wasu iyaye da aka zanta dasu sun bayyana irin kokarin da suka yi.Malam Umar Faruk ya ce yana da mata biyu kuma ko yaushe ya bar gida ya kan fada masu da zara an zo ba da allurar rigkafin polio su tabbata sun mika ‘ya’yansu an yi masu.

Ita ko Jamila Bello cewa ta yi duk wadanda ba sa kai ‘ya’yansu a basu allurar yakamata a nanata masu su rika kai yaransu saboda idan basu kaisu ba suna haduwa da yaran da suka samu allurar a makaranata, cikin unguwanni da wurin wasa. Cututukan da wadanda basu da allurar ke dashi na iya sahafar wadanda suka karbi allurar.

Wani ya bada shawarar cewa idan ana so a shawo kan wannan matsala, tilas ne a yi anfani da shugabannin al’umma da na addini, domin a shawo kawunan iyayen da har yanzu basu yadda da allurar ba.

A saurari rahoton Hauwa Umar domin karin bayani

[ad_2]

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...