NEMA ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo dasu gida daga ƙasar Chad

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA ta ce ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo da su bayan da su ka maƙale a ƙasar Chad.

A wata sanarwa ranar Laraba hukumar ta ce ƴan Najeriyar da aka dawo da su sun haɗa da yara 71 mata 48  jarirai 8 da kuma maza  23..

Hukumar ta ce waɗanda aka dawo da su sun sauka a filin jirgin saman Murtala Muhammad dake Lagos ranar Talata 08:30 na dare.

Hukumar kula da ƴan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya ita ce ta taimaka wajen kwaso mutanen.

Jirgin saman kamfanin Air Cargo mai  rijistar namba SU-BUR shi ne ya sauke mutanen a filin jirgin saman na Murtala Muhammad dake Ikeja da ƙarfe 08:30 na dare.

Wasu daga cikin mutanen sun bayyana jin daɗinsu kan nasarar da aka samu ta dawo da su gida lafiya.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...