Shugaba Bola Tinubu zai gabatar da kasafin kudin 2024 ga majalisar dokokin kasar nan da makonni biyu masu zuwa.
Shugaban zai kuma mika karin kasafin kudin na shekarar 2023 ga majalisar dokokin kasar domin tantancewa.
Shugaban kwamitin majalisar dattawa kan kasafin kudi, Sanata Solomon Adeola, wanda ya bayyana hakan yayin taron kaddamar da kwamitin ya bayyana cewa majalisar kasar za ta tabbatar da cewa an zartar da kasafin kudin shekarar 2024 kafin ranar 31 ga watan Disamba, 2024.