[ad_1]
Kungiyar likitoci ta Medecins Sans Frontieres ta ce ta kaddamar da taimakon gaggawa a arewa maso gabashin Najeriya bayan mutuwar yara akalla 33 a sansanin ‘yan gudun hijira da ke Borno.
MSF ta ce yaran sun mutu ne tsakanin ranakun 2 zuwa 15 ga watan Agusta a sansanin ‘yan gudun hijirar da ke Bama a Jihar Borno.
An kiyasta cewa akwai yara kusan dubu shida ‘yan kasa da shekara 5 a sansanin da ke fuskantar wannan barazanar.
MSF ta ce a yanzu ta soma ba da tallafin gaggawa na abinci mai gina jiki, da magunguna tsakanin yaran da ke sansanin.
Ana dangata yanayin damina da karuwar matsalolin lafiya irinsu zazzabin cizon sauro da sauran cututtuka masu yaduwa a sansanin.
Sai dai Hukumar bada agajin gaggawa NEMA ta ce tana sane da karuwar tamowa a sansanin na Bama, amma ta musanta mutuwar adadin wadanan yara kamar yadda MSF ke cewa.
[ad_2]