
Nafiu Bala jigo a jam’iyar ADC ya jagoranci zanga-zangar magoya bayansa ya zuwa ofishin hukumar zabe ta INEC dake Abuja a ranar Alhamis.
Bala na ikirarin cewa shi ne halastaccen shugaban jam’iyar ADC inda ya ke ƙalubalantar shugaban jam’iyar David Mark a gaban kotu.
Zanga-zangar tasa na zuwa ne kwana guda bayan da tsagin Mark su ka gudanar da zanga-zangar lumana irinta a ofishin INEC.
A yayin zanga-zangar ta yau Bala ya yi kira ga INEC da ta amince da shi a matsayin halastaccen shugaban ADC kamar yadda hukuncin kotu ya tabbatar.
Ya ce ɓangaren Mark na kokarin kwace iko da jam’iyar ta haramtacciyar hanya.
A ranar 1 ga watan Afirilu ne hukumar zabe ta INEC ta janye amincewar da ta yi wa ɓangaren David Mark a matsayin shugabannin jam’iyar ADC biyo bayan wani hukunci da kotun daukaka kara ta yanke.
Hukumar zaben ta ce baza ta sanya idanu ba kan zabubbukan cikin gida na jam’iyar daga kowane tsagi har sai kotu ta yanke hukunci.

