NAFDAC Ta Kama Tan 140 Na Magungunan Da Suka Lalace a Aba

Hukumar NAFDAC ta bankado wuraren ajiya guda biyu da ke cike da magungunan da suka lalace a titin Sam Mbakwe, Aba da ke jihar Abuja.

Wasu daga cikin magungunan an sake liƙe musu sabon lakabin kwanan watan lalacewa kafin jami’an tsaro su isa wurin.

Haka nan a karamar hukumar Osisioma, hukumar ta kwace tan 140 na magungunan da suka lalace, baya ga wasu da aka kama a kasuwar Ariaria.

An kuma tattara samfurin magunguna 178 don gwaji.

NAFDAC ta sha alwashin ci gaba da yaki da safarar magungunan da ke barazana ga lafiya.

More from this stream

Recomended