[ad_1]
Wani ginin shago mai hawa uku da ake kan ginawa ya ruguzo a yankin Jabi dake Abuja inda ya kashe mutum daya tare da rufe wasu 12 a ciki.
Lamarin yafaru ne da misalin ƙarfe 1:30 na rana, cikin wadanda ginin ya binne an samu nasarar ceto mutane 8 ciki har da injiniyan dake kula da aikin wanda aka rawaito ƙafarsa ta karye.
Ya zuwa yanzu dai ana cigaba da aikin ceto ragowar mutanen da suka makale.
Jami’an hukumar birnin tarayya, Abuja dana hukumar bada agajin gaggawa ta kasa NEMA da kuma na hukumar kashe gobara ta tarayya na can na aikin ganin an ceto mutanen.
[ad_2]