Mutum daya ya mutu wasu yara kuma sun makale bayan da gini mai hawa uku ya ruguje a Abuja

[ad_1]








Wani ginin shago mai hawa uku da ake kan ginawa ya ruguzo a yankin Jabi dake Abuja inda ya kashe mutum daya tare da rufe wasu 12 a ciki.

Lamarin yafaru ne da misalin ƙarfe 1:30 na rana, cikin wadanda ginin ya binne an samu nasarar ceto mutane 8 ciki har da injiniyan dake kula da aikin wanda aka rawaito ƙafarsa ta karye.

Ya zuwa yanzu dai ana cigaba da aikin ceto ragowar mutanen da suka makale.

Jami’an hukumar birnin tarayya, Abuja dana hukumar bada agajin gaggawa ta kasa NEMA da kuma na hukumar kashe gobara ta tarayya na can na aikin ganin an ceto mutanen.




[ad_2]

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...