Akalla mutane 30 ne suka rasa rayukansu a wani mummunan hatsarin mota da ya faru a Kwanar Barde, karamar hukumar Gezawa a Jihar Kano, a safiyar jiya. Rahotanni sun ce hatsarin ya shafi wata tirela mai zuwa Gujungu, wadda ta yi hatsari sakamakon tukin ganganci, lamarin da ya jikkata wasu da dama.
Mai magana da yawun gwamna, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya bayyana cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi addu’ar rahamar Allah ga mamatan kuma ya roki Allah ya ba iyalansu hakuri da juriya. Haka kuma, ya yi addu’a ga wadanda suka jikkata domin samun sauki cikin gaggawa.
Gwamna Yusuf ya umarci Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kano da ta tabbatar cewa duk wanda ke asibiti sakamakon hatsarin ya samu kulawa kyauta ba tare da jinkiri ba. Hakanan, ya umarci Ofishin Mai Ba da Shawara Kan Harkokin Jin Kai da ya duba hatsarin nan da nan tare da shirin tallafawa iyalan mamatan.
Gwamnan ya kuma gargadi direbobin manyan motoci da su guji tukin ganganci, tare da bin dokokin hanya domin kauce wa irin wannan masifar nan gaba.
Mutum 30 Sun Gamu Da Ajalinsu Bayan Mummunan Hatsarin Mota A Kano

