[ad_1]
Mutane uku ne suka kone kurmus wasu 5 kuma suka jikkata a wani hatsarin mota a garin Zariagi dake kan babbar hanyar zuwa Lokoja da safiyar ranar Alhamis.
Jami’in wayar da kan jama’a a hukumar kiyaye hatsura ta kasaFRSC, Bisi Kazeem wanda ya tabbatar da faruwar lamarin ya ce ya faru ne safiyar ranar Alhamis.
Ya ce mutane 9 da kuma motoci kirar Toyota Carina, Scania Truck da kuma wata tankar mai lamarin ya rutsa da su.
Wani mutum ya tsira daga hatsarin ba tare da ko kwarzane ba ya dora laifin faruwarsa kan gudun wuce sa’a.
“Wadanda suka mutum sun kone tare da motocin waɗanda suka ji rauni kuma an ɗauke su zuwa cibiyar kula da lafiya ta tarayya dake Lokoja.”
Ya ce tawagar masu ceto na hukumar ta FRSC da suka isa wurin bayan da hatsarin ya faru sun shiga ɗebe motocin daga kan titunan.
[ad_2]