Mutane sama da 50 sun mutu a gobarar da ta tashi a haramtacciyar matatar mai a Imo

Mutane da yawansu ya tasamma 100 ne suka mutu a wata gobara da ta tashi a wasu haramtattun matatun mai biyu dake kusa da juna a jihar Imo dake yankin Niger Delta.

Lamarin ya faru ne ranar Juma’a da daddare bayan da aka samu fashewar wani abu a matatun.

Gobarar ta ƙone akasarin mutanen da ta rutsa da su ta yadda ba a iya gane su. Waɗanda lamarin ya ritsa da su sun haɗa da masu gudanar da matatar da kuma wasu mazauna yankin.

Kawo yanzu dai babu wata sanarwa daga hukumomi kan musabbabun ta shin gobarar.

More News

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...

Mutane 18 sun ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota

Aƙalla fasinjoji 18 ne suka ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota da ya faru akan babbar hanyar Ojebu-Ode zuwa Ore a yankin Ogbere dake...

AMBALIYA: Bafarawa ya ba wa al’ummar Sokoto gudunmawar naira biliyan 1

Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Alhaji Attahiru Bafarawa, ya bayar da gudummawar Naira biliyan daya ga al’ummar Sokoto, domin rage radadin wannan annoba.An bayyana hakan...

Ƴanbindiga sun kai hari coci-coci a Kaduna, sun kuma yi garkuwa da mutane

Mutane 3 ne ake fargabar sun mutu, sannan an yi garkuwa da wasu 30 bayan wani hari da wasu ‘yan bindiga suka kai a...