Mutane 74 sun kamu da cutar zazzaɓin Lassa cikin mako guda – NCDC

Hukumar NCDC dake yaki da cututtuka masu yaɗuwa ta tabbatar da cewa mutane 74 ne suka kamu da cutar zazzaɓin Lassa a makon da ya wuce.

A jihohi 9 ne aka samu karin mutanen da suka kamu da cutar mai haɗarin gaske inda jihar Ondo take kan gaba da yawan mutane.

Mutane 28 ne suka kamu da cutar a jihar Ondo sai jihar Bauchi da Edo dake da mutane 18 kowaccen su.

Sauran jihohin da aka samu bullar cutar sun hada da Oyo (3), Ebonyi(3), Benue(1),Katsina(1),Taraba(1) da kuma Kaduna(1).

Cutar zazzaɓin Lassa na hatsari sosai inda take da saurin kisan waɗanda suka kamu da ita.

More News

DA ƊUMI-ƊUMI: DSS sun cafke Sowore a filin jirgin na Legas

Jami'an Hukumar Ƴansandan Farin-kaya ta DSS sun kama Omoyele Sowore, jagoran kungiyar  #RevolutionNow Movement da ke adawa da gwamnati a filin jirgin sama na...

Ƴan bindiga sun ƙone ginin hedkwatar ƙaramar hukuma tare da kashe jami’an tsaro

Ƴan bindiga sun kai farmaki hedkwatar ƙaramar hukumar, Isiala Mbano dake jihar Imo da tsakar daren ranar 3 ga watan Satumba inda suka ƙone...

An kama wasu ƴanta’adda da ke da alaƙa da Turji

Akalla mayaka 18 da ke da alaka da fitaccen shugaban ‘yan ta’adda Bello Turji aka kama a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin...

Dakarun Najeriya sun kai farmaki wa ƴan’adda a Borno, wani kwamanda ya miƙa wuya

Rundunar sojin Najeriya ta sanar a ranar Lahadin cewa dakarunta sun yi nasarar kashe wani fitaccen kwamandan kungiyar Boko Haram, Abu Rijab da wasu...