
Mutanen da basu gaza 7 ne suka rasa rayukansu a wani hatsarin mota da ya faru akan hanyar Kaltungo-Cham dake jihar Gombe.
Mr Samson Kaura kwamandan shiyar Gombe na Hukumar Kiyaye Afkuwar Hatsura ta Ƙasa FRSC shi ne ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya ce wasu mutane 35 sun samu raunuka iri daban-daban a hatsarin da ya rutsa da wata babbar mota ƙirar tirela da ya faru da misalin ƙarfe 07:10 na safe.
Kaura ya dora alhakin hatsarin kan shanyewar birkin motar dake ɗauke lemukan roba da kuma mutane 38 da su ka haɗa da maza 34 da ƙananan yara 2.
Ya ce waɗanda su ka mutu sun haɗa maza biyar da kananan yara mace da namiji ya ƙara da cewa an miƙa gawarwakin babban asibitin Kaltungo.