Mutane 17 sun jikkata wasu biyu sun mutu a hatsarin tirela a Abuja

Mutane biyu sun rasa rayukansu a yayin da wasu 17 suka samu nau’in raunuka daban-daban bayan da wata motar tirela ta fadi a wurin wani shingen binciken sojoji dake kan babbar hanyar Abuja zuwa Lokoja.

Wani shedar gani da ido ya ce hatsarin da ya faru da misalin ƙarfe 1:23 na dare ya rutsa da wata motar tirela dake ɗauke da siminti wacce ta jirkice ta faɗi a kusa da shingen binciken.

Ya ce direban ya tawo ne daga wajejen Lokoja dauke da fasinjoji dake zaune akan simintin da ya ɗauko lokacin da motar ta ƙwace ta ci karo da wata katangar kankare da sojojin suka gindaya abun da ya tilasta mata faduwa.

Ya ce mutum guda ya mutu nan take a yayin da wani guda ya maƙale a cikin simintin tuni aka kai sauran gawarwakin ya zuwa asibitin Abaji .

Wani jami’in hukumar FRSC kiyaye afkuwar hatsura ta ƙasa  wanda aka yi aikin ceto mutanen da shi da ya nemi a ɓoye sunansa ya tabbatar da faruwar lamarin.

More from this stream

Recomended