[ad_1]
Garba Salisu, daraktan sashen agaji a hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Niger ya ce ya zuwa yanzu mutane 14 ne suka mutu sanadiyar ambaliyar ruwa da ta faru a sassa daban-daban na jihar.
A wata tattaunawa da kamfanin Dillancin Labaran Najeriya, NAN ranar Asabar, ya ce hukumar ta dauki kwararru da suka iya ruwa su 200 domin su taimaka wajen aiyukan ceto.
Salisu ya roki mazauna jihar da su guji gini kan hanyoyin ruwa kana su daina zubar da shara barkatai domin gujewa illar ambaliyar ruwa.
“Babban abinda nafi tsoro shine yawancin ruwan da ake yi na dare ne lokacin da mutane suke bacci amma mafita ɗaya ce shine samar da muhalli da zai tabbatar da wucewar ruwa ba tare da tsaiko ba.”ya ce
Daraktan ya yi kuma kira ga al’ummomin dake wuraren dake yawan samun ambaliyar ruwa da su kauracewa wuraren na wucin gadi domin kaucewa masifa.
[ad_2]