Mutane 13 sun ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota

Hukumar kiyaye afkuwar hatsura ta ƙasa FRSC ta ce mutane 13 ne suka mutu a wani hatsarin mota akan titin Owo-Ikare dake jihar Ondo.

A wata sanarwa da aka fitar ranar Asabar, Samuel Ibitoye shugaban hukumar a jihar Ondo ya ce hatsarin ya rutsa da wata mota dake ɗauke da atamfofi da yaduka da kuma  wata motar bass dake ɗauke da fasinjoji 14.

Jumillar mutane 14 hatsarin ya rutsa da su 13 daga cikinsu suka ƙone ƙurmus a yayin da aka ceto mutum guda shi kaɗai da ya samu munanan raunuka.

“Wani shedar gani da ido ya bayyana cewa motar bass din na tawowa daga wajen Ikare sai tayarta ta fashe inda ta ƙwace ta ci karo da da ɗaya motar da ta fito daga wajen Owo. Suna cin karo da juna suka kama da wuta,” a cewar sanarwar.

Ibitoye ya ce jami’an hukumar FRSC da jami’an ƴan sanda da na hukumar kashe gobara sun yi gaggawar isa wurin inda suka fara aikin ceto.

Ya ce waɗanda suka jikkata an garzaya da su Cibiyar Kula Da Lafiya ta Tarayya dake Owo.

More from this stream

Recomended