Mutane 11 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

Mutanen da basu gaza 11 ne ba aka tabbatar da sun mutu a yayin da wasu 16 suka jikkata mutum ɗaya kuma ya tsira ba tare da ko ƙwarzane ba a wani mummunan hatsarin mota a mahaɗar Gaya dake kan titin Kano-zuwa Maiduguri.

Kwamandan shiyar  Kano na hukumar FRSC dake kiyaye afkuwar  haɗura ta ƙasa, Ibrahim Sallau-Abdullahi shi ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar Abdullahi Labaran ya fitar a ranar Asabar.

Ya ce hatsarin ya rutsa da motoci biyu É—aya Toyota Hummer mai namba KTG 190 XB  da kuma wata Æ™aramar motar a kori kura Æ™irar Hijet mai namba KTG 501 YG.

“Mun samu kira da misalin Æ™arfe 03:45 na rana a ranar  19 ga watan Afrilu munyi gaggawar tura jami’an mu tare da motar su zuwa wurin domin ceto mutanen da abun ya shafa dai-dai Æ™arfe 03:55,”Abdullahi ya ce.

Kwamandan ya ce hatsarin ya faru ne sakamakon gudun wuce sa’a da ya kai ga motocin sun yi tawo mu gama suka kuma kama da wuta.

“Hatsarin ya rutsa da mutane 28 dake cikin motocin biyu 11 suka mutu a ciki wasu 16 suka jikkata aka kuma ceto mutum 1 ba tare da ko Æ™warzane bai yi ba,”.

Abdullahi ya ce an yiwa gawar mutanen jana’iza aka bunne su tare a yayin da aka kai waÉ—anda suka jikkata Asibiti.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...