Mutane 11 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

Mutanen da basu gaza 11 ne ba aka tabbatar da sun mutu a yayin da wasu 16 suka jikkata mutum ɗaya kuma ya tsira ba tare da ko ƙwarzane ba a wani mummunan hatsarin mota a mahaɗar Gaya dake kan titin Kano-zuwa Maiduguri.

Kwamandan shiyar  Kano na hukumar FRSC dake kiyaye afkuwar  haɗura ta ƙasa, Ibrahim Sallau-Abdullahi shi ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar Abdullahi Labaran ya fitar a ranar Asabar.

Ya ce hatsarin ya rutsa da motoci biyu É—aya Toyota Hummer mai namba KTG 190 XB  da kuma wata Æ™aramar motar a kori kura Æ™irar Hijet mai namba KTG 501 YG.

“Mun samu kira da misalin Æ™arfe 03:45 na rana a ranar  19 ga watan Afrilu munyi gaggawar tura jami’an mu tare da motar su zuwa wurin domin ceto mutanen da abun ya shafa dai-dai Æ™arfe 03:55,”Abdullahi ya ce.

Kwamandan ya ce hatsarin ya faru ne sakamakon gudun wuce sa’a da ya kai ga motocin sun yi tawo mu gama suka kuma kama da wuta.

“Hatsarin ya rutsa da mutane 28 dake cikin motocin biyu 11 suka mutu a ciki wasu 16 suka jikkata aka kuma ceto mutum 1 ba tare da ko Æ™warzane bai yi ba,”.

Abdullahi ya ce an yiwa gawar mutanen jana’iza aka bunne su tare a yayin da aka kai waÉ—anda suka jikkata Asibiti.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...