[ad_1]
Kimanin Musulmin Australia 30,000 ne suka taru a birnin Sydney ranar Talata inda suka yi sallar rokon ruwa sakamakon mummunan farin da ba a taba fuskantar irin sa ba a kasar.
Masallata daga manyan masallatai 16 ne suka hadu wuri guda “domin nuna goyon baya da ba da hadin kai” ga manoma da sauran mutanen da farin ya shafa.
An yi sallar ne lokacin da aka gudanar da babbar sallah sannan aka yanka dabbobi.
An kaddamar da wata gidauniyar tallafa wa manoman da farin ya shafa.
Kungiyar Musulmi ‘yan kasar Lebanon da ke masallacin Lakemba na yammacin Sydney ce ta kaddamar da gidauniyar.
“A matsayinmu na ‘yan uwa daya ‘yan kasar Australia, muna ganin ya kamata mu bayar da tamu gudunmawar da goyon baya ga mabukata,” in ji shugaban kungiyar Samier Dandan.
“Wannan ne lokacin da ya kamata mu hada kai mu tallafawa wadanda ke cikin mawuyacin hali.”
Daraktan kungiyar, Ahmad Malas, ya shaida wa BBC kowa ya ji dadi lokacin da aka kaddamar da gidauniyar.
Ya kara da cewa ana yin sallar rokon ruwa ce idan ana kamfar ruwan sama.
[ad_2]