
Gwamnatin Tarayya ta nuna rashin gamsuwar ta da yadda ake samun sabani tsakanin matakan da take dauka kan yaki da Corona virus da kuma matakan da wasu jihohi ke dauka a nasu bangaren.
A Jiya ne shugaba Muhammadu Buhari ya tattauna da wasu gwamnonn jihohi ta Intanet kan batun yaki da cutar Corona da kuma batutuwan da suka shafi tattalin arziki da tsaro.
Sai dai Shugaba Buhari ya nemi hadin kan jihohin, inda ya ce gwamnatin Tarayya na tufka wasu jihohin na warwarewa.
A tattaunawarsa da BBC mai magana da yawun shugaban kasa Malam Garba Shehu ya bayyana cewa abin takaici ne a ce gwamnati tana daukan matakan yaki da annoba amma ana samun matsalar hadin-kai.
Ya ce ”ba wai zargi mu ke yi ba ko kushe, amma akwai bukatar a ce ana tafiya tare saboda idan matsaya ba ta zo guda ba, da wuya a yi nasara a yaki da Coronavirus.
Malam Garba, ya ce kwamitin da ke yaki da annobar na kasa na kokawa kan yadda matakan wasu jihohi ke warware nasarorin da ake samu akan annobar.
Yace kamata ya yi kafin a dau kowanne irin mataki to a tuntubi masana don neman shawarwari”
Yakara da cewa ba wai ana ganin babu hadin-kai daga gwamnoni ba ne, sai dai lura da cewa kowacce jiha ita ke daukan nata matakin akwai bukatar a rinka aiki da shawarwarin kwararu.