Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya bayyana cewa ƙasarsa ba za ta shiga yaƙi da Iran ba, duk da matsin lambar da yake fuskanta daga shugaban Amurka, Donald Trump.
Starmer ya bayyana hakan ne yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a yau. Ya ce akwai matsin lamba mai yawa da ake yi masa domin ya sauya matsayinsa, amma ya jaddada cewa ba zai yi hakan ba.
Ya ƙara da cewa a matsayinsa na Firaminista, zai ci gaba da yanke shawara ne bisa muradun ƙasar Birtaniya, ba tare da tasirin waje ba.
Lokacin da aka tambaye shi ko rikicin da ke tsakaninsa da Trump zai sa ya ƙara kusantar Turai, Starmer ya ce ba zai fifita wata ɓangare ɗaya ba. Ya ce, “Yana da muhimmanci a gare mu mu ci gaba da samun kyakkyawar alaƙa da Amurka da kuma Turai baki ɗaya.”
A wani ɓangaren kuma, Trump ya shaida wa jaridar The Telegraph cewa yana duba yiwuwar ficewar Amurka daga ƙungiyar tsaron NATO da muhimmanci.
Shugaban na Amurka ya kuma zargi NATO da Birtaniya da rashin goyon bayan yaƙin da ƙasarsa ke yi da Iran, lamarin da ya ƙara tsananta saɓanin da ke tsakaninsu.
“Mu Ba Za Mu Shiga Yakin Da Kuke Yi Da Iran Ba, Duk Da Matsin Lamba”, Firaministan Birtaniya Ya Faɗa Wa Trump

