Ya zuwa wannan lokaci babu cikakken bayani kan dalilin da ya sa ta ajiye aikin.
Sannan babu karin haske kan yaushe ta mika takardar murabus din.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa wani na kusa da minista Adeosun ya tabbatar da cewa ta ajiye aikin.
Rahotanni har ila yau na nuni da cewa, murabus din ministar, ba zai rasa nasaba da abin fallasa da ya bayyana cewa takaradar shaidar shirin yi wa kasa hidima na NYSC da ta mallaka na bogi ne.
“Mun samu tabbacin cewa, ta (Adeosun) ajiye aikinta” Inji jaridar Vanguard, ko da yake jaridar ta ruwaito cewa, mataimakan ministar, sun musanta hakan.
Binciken da jaridar Vanguard ta ce ta gudanar kan lamarin, ya nuna cewa, jami’an fadar gwamnati sun yi ta kiran makusantan ministar, domin neman karin bayani kan wannan lamari, kamar yadda ta wallafa a shafin yanar gizonta a yau Juma’a.
Adeosun ta yi ta fuskantar matsin lamba kan ta yi murabus, bayan da bincike ya gano cewa takaradar shaidar ta bogi ce.
Masu lura da al’amura sun ce, ta yiwu Adeosun ta ajiye aikinta ne domin kada ta shafawa shugaba Buhari kashin kaji, a yunkurin da yake yi na neman wa’adi na biyu a zaben badi.