Ministar Kudi Kemi Adeosun Ta Yi Murabus

Rahotanni daga Najeriya na cewa, Ministar kudi, Kemi Adeosun, ta ajiye mukaminta.

Ya zuwa wannan lokaci babu cikakken bayani kan dalilin da ya sa ta ajiye aikin.

Sannan babu karin haske kan yaushe ta mika takardar murabus din.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa wani na kusa da minista Adeosun ya tabbatar da cewa ta ajiye aikin.

Rahotanni har ila yau na nuni da cewa, murabus din ministar, ba zai rasa nasaba da abin fallasa da ya bayyana cewa takaradar shaidar shirin yi wa kasa hidima na NYSC da ta mallaka na bogi ne.

Adeosun ta yi ta fuskantar matsin lamba kan ta yi murabus, bayan da bincike ya gano cewa takaradar shaidar ta bogi ce.

Masu lura da al’amura sun ce, ta yiwu Adeosun ta ajiye aikinta ne domin kada ta shafawa shugaba Buhari kashin kaji, a yunkurin da yake yi na neman wa’adi na biyu a zaben badi.

More News

Ƴansanda sun kama muggan ƴan fashi da makami

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Elemoro reshen jihar Legas sun kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a fashi da makami a...

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riÆ™aƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 Æ™irar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...