Rahotanni daga Najeriya na cewa, Ministar kudi, Kemi Adeosun, ta ajiye mukaminta.
Ya zuwa wannan lokaci babu cikakken bayani kan dalilin da ya sa ta ajiye aikin.
Sannan babu karin haske kan yaushe ta mika takardar murabus din.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa wani na kusa da minista Adeosun ya tabbatar da cewa ta ajiye aikin.
Rahotanni har ila yau na nuni da cewa, murabus din ministar, ba zai rasa nasaba da abin fallasa da ya bayyana cewa takaradar shaidar shirin yi wa kasa hidima na NYSC da ta mallaka na bogi ne.
Adeosun ta yi ta fuskantar matsin lamba kan ta yi murabus, bayan da bincike ya gano cewa takaradar shaidar ta bogi ce.
Masu lura da al’amura sun ce, ta yiwu Adeosun ta ajiye aikinta ne domin kada ta shafawa shugaba Buhari kashin kaji, a yunkurin da yake yi na neman wa’adi na biyu a zaben badi.