Tsohon gwamnan jihar Ondo, Olusegun Mimiko ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa a shekarar 2019.
Mimiko ya ce zai tsaya takara a karkashin jam’iyyar Labour Party (LP).
Ya bayyana aniyar tasa ranar Laraba lokacin da ya ziyarci ofishin jam’iyar na kasa dake Abuja.
Toshon gwamnan ya ce idan suka cigaba da tsayawa a gefe to kashe dake faruwa a yankin arewa ta tsakiya da kuma wasu sassa na kasarnan zai iya mamaye kasar baki daya.
Ya kuma kara da cewa matsalar tattalin arziki da ake fama da ita a yanzu tamkar somin tabi ne kan abinda zai faru anan gaba.
Mimiko ya mulki jihar Ondo na tsohon shekaru 8 karkashin jam’iyar LP kafin ya koma jam’iyar PDP.
Ya kuma sake komawa jam’iyar ta Labour a shekarar 2018.