Mece ce makomar Pogba da Karius da Rabiot da Mario da Norwood da kuma Bakayoko?

[ad_1]

Tiemoue Bakayoko

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Tiemoue Bakayoko

AC Milan tana hakon dan wasan Chelseadan kasar Faransa mai shekara 23, Tiemoue Bakayoko, domin ya buga wasan aro, wanda zai zama kwantiragi na din-din-din, in ji (Sun).

Barcelona za ta nemi Paul Pogba bayan an rufe kasuwar musyaar ‘yan wasa ta Turai ranar 31 ga watan Agusta, bayan ta “amince a asirce” cewar Manchester United ba za ta sayar da dan wasan Faransan mai shekara 25 ba a cikin wannan watan, in ji (Telegraph).

Golan Liverpool Loris Karius, mai shekara 25, dan wasa ne da Besiktas ke hako. Kungiyar ta Turkiyya tana son dan kasar Jamus din ya buga mata wasan aro a tsawon kaka daya, in ji (Sun).

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Raheem Sterling

Kawo yanzu dai dan wasan Ingila, Raheem Sterling, bai yarda ya tsawaita kwantiraginsa ba da Manchester City ba, yayin da kocin kungiyar Raheem Sterling ya ce kungiyar “tana jin dadinsa kuma za ta so Raheem ya tsaya”, in ji (Telegraph).

KocinChelsea Maurizio Sarri ya ce dan wasan baya David Luiz yana da “babbar makoma” a kulob din , duk da cewa dan kasar Barazil din mai shekara 31 ba ya samun gurbin wasa sosai karkashin tsohon kocin kulob din Antonio Conte, in ji (Mirror).

Sarri ya ce ya yi nadamar rashin saya wa Chelsea Gonzalo Higuain, amma dan kasar Argentina din mai shekara 30 ya ce ya koma AC Milan ne daga Juventus domin Sarri “kadai ne yake so na a Chelsea” amma kuma “a Milan kowa na so na”, in ji Star

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Jason Denayer

Dan wasan tsakiyar Tottenham dan kasar Ingila Dele Alli ya ce ababen da ke tafiya a kulob din ba su yi tasiri kan ‘yan wasan ba bayan Spurs ba ta sayi ko dan wasa daya ba a kasuwar musayar ‘yan wasan lokacin bazara da aka rufe kwanan nan, in ji (Mail).

Dan wasan bayan Manchester City mai shekara 23 Jason Denayer ya ki ya je ya buga wasan aro domin dan wasan bayan Belgium din yana son ya koma kungiyar kwallon kafar Turkiyya, Galatasaray, in ji(Star).

Keftin din Portugal, Cristiano Ronaldo, ya bukaci Juventus ta nemi dan wasan tsakiyar Lazio Sergej Milinkovic-Savic. An alakanta dan wasan mai shekara 23 dan kasar Serbiya da komawa Manchester United da Chelsea, in ji (Star).

Dan wasan tsakiyar Paris St-Germain Adrien Rabiot, mai shekara 23, ya ki tayin tsawaita kwatiraginsa da zakarun gasar Ligue 1. Kwantiragin dan wasan Faransan zai kare a karshen wannan kakar ,in ji (L’Equipe – in French).

Dan wasan bayan Schalke dan kasar Jamus Thilo Kehrer, mai shekara 21, ya shirya domin komawa Paris St-Germain bayan an cimma yarjejeniyar fan miliyan 33, in ji (Guardian).

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Joao Mario

Real Betis za ta iya tayin sayen dan wasan kungiyar Inter Milan, Joao Mario. Dan wasa tsakiyar Portugal din, mai shekara 25 ya buga wasanni 14 a lokacin da ya je buga wasan aro a West Ham United a kakar da ta gabata da gasar kofin duniya, in ji (Mundo Deportivo).

Dan wasan tsakiyar Watford dan kasar Faransa Abdoulaye Doucoure, mai shekara 25, ya nuna cewar zai bar kulob din a gaba, in ji (Watford Observer).

Rahotanni sun ce Manchester United na tattaunawa da Fenerbahce kan dan wasan bayan Argentina mai shekara 28, Marcos Rojo, in ji (Mirror).

[ad_2]

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...