Mece ce makomar Eriksen da Pogba da Nzonzi da Loftus-Cheek da kuma Darmian?

[ad_1]

Christian Eriksen

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Christian Eriksen

Paris St-Germain tana shirin ataya dan wasan Tottenham mai shekara 26 wanda shi ne madugun kasar Denmark Christian Eriksen, kan kudi fan miliyan 100, in ji (Express).

PSG tana kuma son wani dan wasan Tottenham kuma – dan wasan bayan Ingila Danny Rose. Spurs ta yarda ta sayar da dan wasan mai shkeara 28 a wannan watan, in ji (Mirror).

Schalke na son daukar dan wasa tsakiyar Ingila mai shekara 22 Ruben Loftus-Cheek domin ya buga mata wasan aro , amma da alama Chelsea ba za ta yarda da tafiyarsa ba, in ji (Telegraph).

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Ruben Loftus-Cheek

Loftus-Cheek ya shirya domin jajircewa wajen samun gurbin wasa a cikin ‘yan wasa 11 na farko na Chelsea, in ji(Guardian).

Shugaban Barcelona Josep Maria Bartomeu bai yanke kaunar neman dan wasan tsakiyar Manchester United dan kasar Faransa Paul Pogba ba, mai shekara 25, kuma ya ce “kawo yanzu dai muna da lokacin ciniki” a kasuwar musayar ‘yan wasa ta lokacin bazara, in ji (Sun).

Marseille na tunanin taya dan wasa tsakiyar Arsenal dan kasar Masar mai shekara 26 Mohamed Elneny, wanda ya rattaba hannu kan wata sabuwar yarjejeniya ta shekara hudu a watan Marais, in ji (Mirror).

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Mario Balotelli

Kocin Nice Patrick Vieira ya ce tsohon dan wasan gaban Manchester City da Liverpool ami shekara 28 Mario Balotelli – dan kasar Italiya – na son barin kulob din, in ji Canal+ .

Dan wasan bayan Manchester United Matteo Darmian yana son tafiya, kuma Juventus da Napoli da kuma Inter Milan na son dan wasan bayan Italiya din mai shekara 28, in ji (Manchester Evening News).

KocinManchester United Jose Mourinho ya shiga rudu game da maganar da Paul Pogba ya yi ta nuna cewar akwai matsala tsakaninsu, in ji (Telegraph).

Liverpool za ta saurari tayi akan dan wasan bayan kasar Estoniya, mai shekara 32, Ragnar Klavan, in ji (Liverpool Echo).

Dan wasan gaban Ivory Coast, Wilfried Zaha, mai shekara 25, ya ce har yanzu yana tattaunawa da Crystal Palace game da tsawaita kwantiraginsa ,in ji (Mail).

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Steven Nzonzi

Paris St-Germain da Monaco suna son dan wasan Sevilla dan kasar Faransa mai shekara 29, Steven Nzonzi, in ji (France Football).

Kocin Real Madrid Julen Lopetegui yana son sayen dan wasan baya da kuma dan wasan gaba kafin a rufe kasuwar musayar ‘yan wasa, in ji(AS).

[ad_2]

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...