Mayakan ISWAP sun kashe Fulani makiyaya 20 a Borno

Akalla Fulani makiyaya 20 ne aka bada rahoton mayakan ISWAP sun kashe a wasu hare-hare da suka kai wasu kauyuka dake jihar Borno.

Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan sha’anin tsaro a yankin tafkin Chadi ya ce yan ta’addar sun kai farmaki kauyen Kukawa inda suka kashe Fulani makiyaya 14 a ranar 25 ga watan Yuli.

Tun da farko yan ta’addar sun saka dokar hana kiwon shanu, noma da kamun kifi a yankunan Kukawa, Doro da kuma Kula.

Jawabin da aka wallafa ya ce yan ta’addar sun yi dirar mikiya a kauyen kan babura kusan 17 inda suka zargi Fulanin da ketare iyaka da kuma yi wa sojan Najeriya leken asiri.

Ya kara da cewa yan ta’addar sun kuma kashe wasu karin makiyaya 6 a wani harin da aka kai a Kukawa duk a rana daya.

Bayan da kura ta lafa mutanen kauyen da suka samu nasarar tserewa sun gano gawarwaki hudu bayan sun dawo garin.

A wani labarin kuma mayakan kungiyar ISWAP sun samu yi garkuwa da wasu fulani makiyaya 7 a harin da suka kai Monguno.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon É—an majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...