Mayakan ISWAP sun kai hari sansanin soja a jihar Yobe

Mayakan kungiyar yan ta’adda ta ISWAP sun kai farmaki garin Buni Gari dake karamar hukumar Gujba ta jihar Yobe da tsakar daren ranar Juma’a.

Harin na zuwa ne kwanaki biyu bayan da gwamnonin shiyar arewa maso gabas suka gudanar da taronsu a garin Damaturu babban birnin jihar inda suka tattauna kan batun matsalar tsaro, talauci da kuma rashin tituna a yankin.

Wata majiyar jami’an tsaro ta tabbatar da faruwar harin inda ya bayyana cewa yan ta’addar sun kona wani sashe na  hedkwatar 27 Tactical Brigade dake garin na Buni Gari.

Buni Gari na da nisan  kilomita 7 daga garin Buni Yadi inda makarantar Zaratan Sojan Najeriya take.

Wasu mazauna garin sun fadawa jaridar Leadership cewa yan ta’addar sun rika harbin kan me uwa da wabi kafin su kona wane sashe na sansanin sojan da kuma wasu gine-gine dake kusa.

Jaridar ta rawaito cewa dakarun sojan Najeriya na rundunar Operation Hadin Kai sun gwabza kazamin fada da maharan a garin na Buni Gari kamar yadda wata sanarwa da rundunar ta fitar ta bayyana.

More from this stream

Recomended