Mayaƙan ISWAP sun kashe kwamandan Boko Haram

Mayaƙan ISWAP sun kashe Gana Alhaji Ali kwamandan Boko dake lura da Sambisa da yankin Gwoza a tsaunukan Gwoza.

Wasu majiyoyi dake jami’an tsaro sun ce Ali na daga cikin hatsabiban mayaƙan Boko Haram a jihar Borno kuma an kashe shi ne a harin kwanton ɓauna da mayakan ISWAP suka kai a ranar Lahadi.

“Shi ne mataimakin Ali Ngulde idan ka ɗauke Abubakar Shekau babu wani mutum da ya kashe mutane kamarsa a dajin Sambisa, Banki da kuma bayan tsaunukan Gwoza.”

Majiyar ta ƙara da cewa yaransa sun dade suna saka fargaba da tsoro a zukatan manoma da kuma matafiya dake bin hanyar Pulka, Gwoza, Bama da kuma Mubi.

More News

Jihar Neja Ta Yi Rajistar Mutane 289 Da Suka Kamu Da Cutar Amai Da Gudawa, 17 Sun Mutu

Wata annobar cutar amai da gudawa a Jihar Neja ta yi sanadin mutuwar mutane 17 tare da kama mutane 289 a kananan hukumomi 11...

An ƙona sakatariyar ƙananan hukumomi 2 a jihar Rivers

Wasu da ake kyautata zaton ɓatagari ne sun ƙona wani sashe na sakatariyar ƙananan hukumomin Eleme da Ikwerre dake jihar Rivers. Ƙona ginin na zuwa...

Ƴanbindiga sun hallaka wani shugaban APC a Kebbi

Wasu ‘yan bindiga sun harbe Bako Bala, shugaban jam’iyyar APC na karamar hukumar Suru a jihar Kebbi, a yayin wani yunkurin yin garkuwa da...

Kotu ta hana VIO kamawa, tsare motoci ko cin tarar direbobi a kan hanya

Justis Evelyn Maha ta Babbar Kotun Tarayya a Abuja ta bayar da umarni da ya hana Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa, wanda aka...