
Aƙalla mayaƙan ƙungiyar ISWAP bakwai ne aka rawaito sun mutu bayan da wani bam da suke ƙoƙarin ɗanawa ya tashi da su a jihar Borno.
Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan sha’anin tsaro a yankin tafkin Chadi ya bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar 30 ga watan Disamba a tsakanin garuruwan Ba’anfani da Koleram dake yankin tafkin Chadi na jihar Borno.
“Wasu majiyoyi sun bayyana cewa an samu fashewa lokacin da ake haɗa bam ɗin da ake tunanin ƴan ta’addan na shirin amfani da shi wajen kai hari a yankin, a cewarsa
Yankin tafkin Chadi ya zama wata matartarar mayaƙan na ISWAP inda a lokuta da dama suke amfani da bam-bamai a yaƙin da suke da jami’an tsaro