Matatar man fetur ta Kaduna za ta dawo aiki a ƙarshen 2024

Ƙaramin ministan albarkun man fetur, Heineken Lokpobiri ya bayyana cewa gyaran gaggawa da ake yiwa matatar man fetur dake Kaduna zai saka ta dawo aiki a karshen shekarar 2024.

A wata sanarwa da kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya fitar Lokpobiri ya ayyana lokacin a yayin ziyarar gani da ido da ya kai domin duba yadda aikin ke cigaba da gudana a ranar Asabar.

Lokpobiri, da shugaban NNPCL Mele Kyari da wasu manyan da daraktocin kamfanin na daga cikin waɗanda suka kai ziyarar ta ranar Asabar.

Ministan ya ce ya bayyana lokacin kammala aikin saboda yadda yaga aikin ke gudana inda ya ce gwamnatin tarayya za ta cigaba da bayar da gudunmawar da ta dace.

Ya ce akwai bukatar gaggawa na ganin matatar ta cigaba da aiki domin cigaban tattalin arzikin kasa da kuma samar da makamashi wanda duka hanya ce ta cigaba mai dorewa.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...