Ƙaramin ministan albarkun man fetur, Heineken Lokpobiri ya bayyana cewa gyaran gaggawa da ake yiwa matatar man fetur dake Kaduna zai saka ta dawo aiki a karshen shekarar 2024.
A wata sanarwa da kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya fitar Lokpobiri ya ayyana lokacin a yayin ziyarar gani da ido da ya kai domin duba yadda aikin ke cigaba da gudana a ranar Asabar.
Lokpobiri, da shugaban NNPCL Mele Kyari da wasu manyan da daraktocin kamfanin na daga cikin waɗanda suka kai ziyarar ta ranar Asabar.
Ministan ya ce ya bayyana lokacin kammala aikin saboda yadda yaga aikin ke gudana inda ya ce gwamnatin tarayya za ta cigaba da bayar da gudunmawar da ta dace.
Ya ce akwai bukatar gaggawa na ganin matatar ta cigaba da aiki domin cigaban tattalin arzikin kasa da kuma samar da makamashi wanda duka hanya ce ta cigaba mai dorewa.