Matasa a Kano, Jigawa da Sokoto za su ci gajiyar tallafin karatu na Tarayyar Turai

An zabi jihar Kano a matsayin daya daga cikin wuraren da za su ci gajiyar sabon shirin samar da ilimi da karfafawa na Tarayyar Turai a wani shirin tallafi a Najeriya.

Shirin na da nufin kara yawan ’yan mata da maza da ke cin gajiyar damar koyo da fasaha masu inganci a jihohin Kano, Jigawa da Sokoto.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da daraktan wayar da kan jama’a na ma’aikatar ilimi ya fitar kuma ya raba wa manema labarai a ranar Talata.

Shugaban tawagar asusun kula da yara na Majalisar Dinkin Duniya, Mista Michael Banda, ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da kwamishinan ilimi na jihar Alhaji Umar Doguwa game da shirin a ofishinsa a ranar Talata.

More News

Ƴansanda sun hallaka masu garkuwa da mutane

Ƴansanda sun hallaka wasu masu garkuwa da mutane uku da ake zargin sun yi yunkurin yin garkuwa da matar wani dan majalisar dokokin jihar...

Ƴansanda a Katsina sun yi nasarar cafke wasu tantiran masu safarar alburusai wa ƴanbindiga

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Juma’a ta sanar da cewa ta kama wasu manyan ‘yan bindiga guda uku tare da kwato manyan...

Tinubu ya amince da mafi karancin albashi na N70,000

Shugaba Bola Tinubu ya amince da N70,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan Najeriya, inda ya yi alkawarin sake duba dokar mafi karancin...

Mutanen Isra’ila sama da rabin miliyan sun tsere saboda yakin Gaza

Mutanen Isra'ila sama da rabin miliyan ɗaya ne suka fice daga ƙasar kuma ba su koma ba a watanni shida na farkon yaƙin Isra'ila...