
Hakkin mallakar hoto
Google
Isabel Dos Santos ta samu makudan kudade ta hanyar gudanar da haramtaccen kasuwanci da kanfanonin da ke hulda da gwamnatin mahaifinta shugaba Dos Santos
Wani binciken kwakwaf da sashen BBC Panorama ya gudanar ya gano cewa macen da tafi kowa ce mace kudi a nahiyar Afrika ta samu kudin ne ta haramtacciyar hanya.
Isabel Dos Santos ta samu makudan kudade ta hanyar gudanar da haramtaccen kasuwanci da kanfanonin da ke hulda da gwamnatin mahaifinta shugaba Dos Santos.
Wadannan kamfanoni na huldar kwangiloli a lokacin da mahaifin nata shugaban Angola Dos Santos ya ke mulki.
An samu tsegumin fitar takardu sama da 700,000 na kasuwancinta daga masu kwarmata bayanai na nahiyar Afrika, kuma sun baiwa kungiyar kwararrun ‘yan jarida masu binciken kwakwaf na kasa-da-kasa.
Takardar da ta saka wa hannu a makon karshe da ta bar aiki da kamfanin Sonagol na gwamnatin Angola
Takardun sun nuna cewa akwai shaidun da ke nuna cewa wasu al’amuran kasuwancin da ta ke gudanarwa akwai alamun cin hanci da rashawa.
An gano cewa mahaifinta da ya shafe shekara 38 yana mulkin Angola yana ba da kwangiloli ga kamfanoni da sharadin ba da kamisho ga ‘ya’yansa kuma Isabel na cikinsu.
Haka ma an gano cewa kamfanin mai na kasar Sonagol, ya bai wa ‘yar tsohon shugaban wata kwangila mai tsoka sosai.
Kashi talatin na ‘Yan Angola na rayuwa da kasa da dala biyu a duk rana
Kuma da kudin kwangilar ne ta sayi kaso 15 na hannun jari a wani kamfanin makamashi na kasar Focugal.
Wannan kwangila ta samar mata da kaso uku bisa hudu na Yuro biliyan daya.
Yanzu haka Isabel na zaune ne a Burtaniya, kuma ta mallaki manyan gidaje masu tsada a kwaryar birnin Landan, tana kuma kasuwanci da kamfanonin man fetur da deman da kuma na sadarwa.
To sai dai Isabel ta musanta sakamakon wannan bincike, inda ta danganta shi da wani bita da kullin siyasa daga gwamnatin Angola.
A halin yanzu Isabel Dos Santos na fuskantar bincike daga hukumomi a Angola kan zargin cin hanci da rashawa, an kuma rike duk wata kaddara da ta mallaka a kasar yayin da ake ci gaba da gudanar da binciken.
A cewar Andrew Feinstein na mujallar Corruption Watch, wannan balli ya nuna irin yadda Isabel Dos Santos ke cin karenta ba babbaka da kudin talakawa.
Ana ganin cewa dadewar mahaifinta kan karagar mulki na tsawon shekara 38 ne ya bata damar gudanar da wadannan huldodi yadda take so.
To amma duk da haka, wasu ‘yan Angola na zargin shugaba mai ci Joao Lourenço da kokarin cimma burinsa na siyasa ta hanyar binciken iyalin wanda ya gada.