Mataimakin Gwamnan Kano Ya Yi Murabus

Mataimakin gwamnan Jihar Kano State, Kwamared Aminu Abdussalam, ya ajiye mukaminsa.

An bayyana hakan ne a ranar Juma’a cikin wata sanarwa da kakakin Kwankwasiyya Movement, Dakta Habibu Sale Mohammed, ya fitar.

Tun da farko, majalisar dokokin jihar Kano ta fara shirin tsige mataimakin gwamnan daga mukaminsa. Haka kuma, wata kotun tarayya da ke zamanta a Kano ta yi watsi da bukatar da ya gabatar domin dakatar da shirin.

Ta kara da cewa matakin da ya dauka bai zo masa da sauki ba, amma an yi shi ne domin kare muradun al’umma da kuma tabbatar da zaman lafiya a harkokin mulki.

More from this stream

Recomended