Masu Garkuwa Da Mutane Sun Sace Mahaifiyar Wani Dan Majalisar Nijar

[ad_1]

Wannan lamari na zuwa ne kwana guda bayan da masu garkuwar suka saki wani ‘dan kasuwa dake hannunsu bayan da ya biya Miliyan 20 na kudin CFA.

Rahotanni sun nuna cewa da missalin karfe 10 na daren ranar Litnin ne ‘yan bindigar suka yi awon gaba da mahaifiyar dan Majalisar Dokokin Nijar mai wakiltar yankin Diffa, Boulou Mahamadou. Sa’o’i kadan bayan da suka saki dan kasuwa, Kaka Touda Goni mamadou, wanda ya fanshi kansa ta hanyar biyan makudan kudade.

Har ya zuwa hada wannan rahotan ‘yan bindigar na ci gaba da garkuwa da wannan mata, yayin da wata majiya ke cewa an fara tattaunawa domin shawo kan wannan al’amari cikin ruwan sanyi.

Ya zuwa yanzu dai babu wani ko wata kungiya da ta fito ta dauki alhakin garkuwar da ake da mutane.

Domin cikakken bayani saurari rahotan Sule Muminu Barma.

[ad_2]

More News

Ƴan sanda sun kama masu sayen kuri’a a zaben gwamnan Edo

Jami'an rundunar Æ´an sandan Najeriya sun kama wasu mutane 9 da ake zarginsu da sayen kuri'a da kuma mallakar kuri'ar da aka riga aka...

Ƴansanda sun kama muggan ƴan fashi da makami

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Elemoro reshen jihar Legas sun kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a fashi da makami a...

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riÆ™aƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 Æ™irar gida...