Masu garkuwa da mutane sun kashe ƴansanda huɗu a Kaduna

[ad_1]








Bayan da aka yi garkuwa da Sheikh Ahmad Adam Algarkawy da kuma sakin sa da aka yi bayan da aka biya kudin fansa.

Rundunar ƴansanda ta tashi haikan domin lalubo wadanda suka aikata haka inda ta samu nasarar kama biyu daga ciki a wani dan kauyen dake cikin Dajin Rigasa a jihar Kaduna.

Ya yin da tawagar jami’an ƴansanda ke kan hanyarsu ta fitowa daga cikin dajin.

Sun fuskanci ruwan wuta daga sauran masu garkuwa da mutanen har ta kai ga sun kashe jami’an ƴansanda hudu daga ciki.

Ƴansandan da suka rasa rayukansu sun haɗa da Insifecta Benard Odibo, Insifecta Abubakar Mamman, Insifecta Haruna Ibrahim da kuma Sajan Emmanuel Istifanus.

Mutane 6 daga cikin masu garkuwa da mutanen suma sun rasa rayukansu ya yin musayar wuta.




[ad_2]

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...