[ad_1]
Bayan da aka yi garkuwa da Sheikh Ahmad Adam Algarkawy da kuma sakin sa da aka yi bayan da aka biya kudin fansa.
Rundunar ƴansanda ta tashi haikan domin lalubo wadanda suka aikata haka inda ta samu nasarar kama biyu daga ciki a wani dan kauyen dake cikin Dajin Rigasa a jihar Kaduna.
Ya yin da tawagar jami’an ƴansanda ke kan hanyarsu ta fitowa daga cikin dajin.
Sun fuskanci ruwan wuta daga sauran masu garkuwa da mutanen har ta kai ga sun kashe jami’an ƴansanda hudu daga ciki.
Ƴansandan da suka rasa rayukansu sun haɗa da Insifecta Benard Odibo, Insifecta Abubakar Mamman, Insifecta Haruna Ibrahim da kuma Sajan Emmanuel Istifanus.
Mutane 6 daga cikin masu garkuwa da mutanen suma sun rasa rayukansu ya yin musayar wuta.
[ad_2]