Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Najeriya (NPA) ta bayyana cewa akalla jiragen ruwa 28 ne ake sa ran za su iso tashoshin jiragen ruwa na Apapa, Tin-Can Island da Lekki Deep Sea Port da ke Jihar Legas tsakanin ranar 10 zuwa 19 ga watan Fabrairu.
Hukumar ta fitar da wannan bayani ne cikin sabon rahoton Shipping Position da ta saki a ranar Talata a Legas.
A cewar hukumar, jiragen ruwa 16 daga cikin wadanda ake sa ran zuwansu jiragen kwantena ne dauke da kayayyaki iri-iri. Sauran jiragen 12 kuma na dauke da danyen mai, man fetur (PMS), dizal, gypsum mai yawa, alkama, blended stock, danyen mai, iskar gas da sauran kayayyaki na gama gari.
Rahoton ya kuma nuna cewa jiragen ruwa da tankokin mai guda 10 sun riga sun iso tashoshin, amma suna jiran samun wurin sauke kaya. Wadannan jirage na dauke da danyen mai, urea, dizal, condensate, fetur, kwantena da sauran kayayyaki.
A gefe guda, NPA ta ce a halin yanzu akwai jiragen ruwa 15 da suke sauke hajojinsu a tashoshin uku da abin ya shafa.
Kayayyakin da ake saukewa sun hada da kayayyaki na gama gari, gypsum, kwantena, taki, sukari, dizal da kuma danyen mai.
Hukumar ta kara da cewa zuwan wadannan jiragen na daga cikin kokarin tabbatar da wadatar man fetur da sauran muhimman kayayyaki a fadin kasar.
Manyan Jiragen Ruwa 28 Za Su Iso Da Man Fetur Da Sauran Kayayyaki Tashar Jiragen Ruwa Da Ke Legas

