Malamai Sun Amince Da Dakatar Da Sallar Juma’a A Kano – AREWA News

Tawagar manyan Malamai a jihar Kano sun amince da dakatar da sallar juma’a a daukacin masallatan jihar, a yayin da dokar hana fita da gwamnati ta saka ke fara aiki a yau Alhamis.

Malaman dai sun gudanar da taron nasu ne a Africa House da ke fadar gwamnatin Kano ranar Alhamis, karkashin kwamitin kar ta
kwana na cutar korona da Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya kafa.

Idan an jima ne dokar hana fita da gwamnatin jihar ta kafa za ta fara aiki, wadda za a shafe tsawon mako guda. Shawararin malaman dai na zuwa ne bayan da hukumomi a jihar Kano
suka sanar da mutuwar wani mutum mai dauke da cutar korona a jihar, yayin da adadin wadanda suka kamu da cutar ya kai mutum 21.

Malaman sun yi nazarin harkokin rayuwar al’umma ne wadanda ke da nasaba da taron
jama’a da nufin bayar da fatawa, inda suka amince da dakatar da Sallar Juma’a a masallatan jihar da kuma tarukan da ake yi da suka shafi karatu a lokacin watan Ramadan, don hana yaduwar cutar korona a tsakanin al’umma.

Dr. Ibrahim Mu’azzam mai Bushira shi ne sakataren karamin kwamitin malamai da kwamitin kar ta kwana na coronavirus ya kafa, wanda ya ce malaman sun amince da a dakatar da gabatar da Sallar Juma’a don gudun kada wani da yake dauke da cutar ya yada ta a tsakanin al’umma.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...