Makomar Guardiola, Neymar, Messi, Mbappe da Ndombele

Hakkin mallakar hoto
Reuters

Manchester City za ta sabunta kwangilar kocinta Pep Guardiola mai tsoka bayan ta yi nasara da karar da ta daukaka kan haramta mata buga gasar zakarun Turai. (Mirror)

Guardiola zai samu kudi kusan fam miliyan £150 domin karfafa tawagarsa. (Guardian)

Dan wasanNapolida Senegal Kalidou Koulibaly, mai shekara 29, yana cikin ‘yan wasan da ake ganin Guardiola zai dauko domin gyra bayansa. (Telegraph – subscription only)

Shugaban Barcelona Josep Maria Bartomeu ya yi watsi da yiyuwar dan wasan Paris St-Germainda Brazil Neymar, mai shekara 28, zai dawo Nou Camp amma ya ce yana diba yiyuwar dauko dan wasan gaba na Inter Milan da Argentina Lautaro Martinez, mai shekara 22. (TV3 via Mundo Deportivo – in Spanish)

Bartomeu ya kuma ce yana da “tabbataci” Lionel Messi, mai shekara 33, zai ci gaba da taka leda a Nou Camp har wuce badi. (TV3 via Evening Standard)

Real Madrid tana da kwarin guiwa kan dan wasan Faransa Kylian Mbappe, mai shekara 21, zai fara tattauna da Paris St-Germain kan batun komawarsa Madrid nan da shekara daya. (Marca)

Liverpool na tunanin sayar da dan wasan bayanta na Croatia Dejan Lovren, mai shekara 31, duk da ya nemi a tsawaita kwantaraginsa. (Goal)

Bayern Munich na shirin taya dan wasan TottenhamTanguy Ndombele, mai shekara 23, da kuma dan tsakiya na Faransa Tiemoue Bakayoko, mai shekara 25, daga Monaco. (Le10Sport via Daily Mail)

Nice ta taya dan wasan Sifaniya mai shekara 24 Rony Lopes daga Sevilla. (RMC Sport – in French)

Brentford na son dan wasan Portsmouthmai shekara 24 Ronan Curtis domin maye gurbinsa da dan wasan Algeria Algerian Said Benrahma. (The News, Portsmouth)

Dan wasan baya na Bournemouth Nathan Ake, mai shekara 25, ba zai sake buga wasa ba a wannan kakar saboda raunin da ya ji a wasa da Leicester. (Bournemouth Echo)

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa É—aya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faÉ—a tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...